Sunday, 30 September 2012

Yaushe kan mage zai waye?


Tsananin son zuciya da tsabagen rashin kishin kasa, sune illolin dake fatattaka zukatan wasu shugabannin Najeriya, har ta kai ma a yanzu babu wani alfanun da ake samu  daga ayyukan da suke zartarwa. Wannan shine dalilin da yasa a maimakon kasar ta ci gaba, kullum sai koma baya ta ke cikin dukkanin al’amuranta.

Tun ana kiran Najeriya ‘Giwar Africa’ tana amsawa, yanzu ce mata ake yi akuyar da ke dauke da takin da ke hana ta motsawa. Ashe dai da gaske ne da gwanayen magana ke cewa, duniya rawar ‘yan mata ce, na gaba kan koma baya. To Najeriya a yau ta zame kashin-baya, ‘yan kannenta duk sun tsere mata fintinkau, har ma tsohon shugaban kasar Ghana, Mr John Kufour, ya fahimci cewa Najeriya ta gaza, don haka a daina cewa da ita Giwar Africa.

Ko wane Shugaba da ya shude, ya taka rawar da walau aka yaba, ko akayi Allah wadai da ita, saboda dangartakansa da masu tatse arzikin kasarsa, Turawan da suka gaji da bautar da kakanninmu, daga bisani suka ba mu mulkin da bai da amfani a gare mu. Tunda bamu iya sarrafa tattalin arzikin kasarmu da kanmu, sai yadda suka ga dama za su ta kankarar mu komai wayyo Allanmu kuma ba za su kyale mu ba.

Amma daga cikinsu babu rawar da aka fi bata ta da tsalle kamar ta Goodluck Ebele Azikwe Mainasara Jonathan. Saboda rashin tabukawar Jonathan wajen ciyar da kasarnan gaba, yanzu gani ake kamar an debe wa manufofinsa ne albarka, domin tun hawansa mulki babu wani abin alfahari guda da ya aiwatar don amfanin jama’arsa. Shugaba Jonathan ya yi alkawurra bila-adadin, amma babu wanda ya cika.

Inda wannan al’amari ya fi ban takaici shine, ta fuskar aikin gona. Ya sha yin alkawurran zai habaka noman rogon da za a rika fitarwa kasashen ketare, amma duk a banza. Kai hasali ma ba kunya ba tsoron jama’arsa, ya karya alkawarin da ya yi cewa, ya daina cin wani burodi idan ba wanda aka yi da rogo ba.

Shugaba Jonathan ya sake daukar wani alkawarin game da noman shinkafa. Ya ce daga shekara mai zuwa gwamnatinsa za ta hana shigowa da shinkafa ‘yar waje, domin a koma cin shinkafa ‘yar Baro, da ake nomawa a kasarnan.

Amma me ya faru?  Ai  cikin ‘yan watanni da yin wannan alkawarin sai ga gogan naka can a Kasar Malawi inda ya kai ziyarar aiki shi da wasu gwamnoni, yana ta buga santi, yayin da yake cin shinkafar da aka noma a can Kasar. Bayan ya cire malafar da ba safai yake cire ta ba, a nan gida Najeriya, ya sosa sankon tsakiyar kansa, sai ya kada baki ya ce da Shugabar Kasar Malawi Mrs Joyce Banda mai masaukinsa: “Daga yau duk wata shinkafa da ni kaina, da jama’ata a Najeriya za su ci, daga nan Kasar za a rika kai mana ita”.

Amma da yake babu wanda zai iya saka masa waiji, sai kawai aka yi masa tafi: “raf-raf-raf”, gogan naka kuwa sai kawai ya fara rausayawa, yana rangwada da wuya kamar wata sabuwar amarya.

To a nan akwai tamabayoyi guda biyu da suka kamata shugaba Jonathan Mai nasara ya amsa, kamar yadda gwamna Isa Yuguda ke kiransa saboda tsabar lusaranci irin na Yuguda. Ta farko ita ce, shin maganar noma wadatacciyar shinkafa a nan cikin gida don kawo karshen wacce Turawa kan noma a wasu kasashe, su shigo mana da ita ta hannun ‘yan barandansu, ta sha ruwan fashi kenan? Sannan  kuma zai cika wancan alkawarin da ya dauka a gaban takwararsa Joyce Banda, game da sayen shinkafar Kasarta, ko kuma santin banza ne ya tafka sakamakon dadin girkin da ya kwasa?

To ko ma dai menene, talakawan Najeriya mun dade da sanin cewa, an kaimu an baro game da aikin gona, tunda gashi ma a bana noman ya gagara saboda ka’idoji masu wahalarwa da aka gindaya don sayar da takin zamani. Dangane da haka da wuya a samu amfanin gona mai albarka a bana daga dan abin da ya rage bayan ambaliyan ruwan da ya halaka gonakin manoman da dama basu samu takin ba.

Wai shin ya zama wajibi ne sai turawa ne za su ciyar da al’ummomin kasar nan da abincin da ake nomawa a wata duniyar can daban? A yanzu ta kai ma a duk shekara sai an kashe Naira miliyan dubu 360, don sayo mana shinkafa daga kasashen ketare. Haka ma akan kashe Naira milayan dubu 180 duk shekara, ko kuma a ce Naira miliyan dari biyar a kullum don sayo alkamar da ake mana burodi ko fanken Karin kumallo. Wadannan ba su ke nan ba, a ko wace shekara kuma sai an kashe Naira miliyan dubu 110, don sayo sukarin da mukan sanya a kunu da koko, ko shayin da muke dunduma kunkuru a ko wace safiya.

Idan da ace wadannan makudan kudade aljifan manoman karkara suke shigewa, ai da tuni sun murmure, sun tayar da komada, sun kuma san zaman rayuwa na armashi suke a Najeriya, ba jirar mutuwa kadai ba.

An dai tabbatar da cewa, ba iya kwanciya aka fi kare ba, sai dai a yi masa gorin mayafi. Ba finmu iya noma, da kasa mai albarka, da matasa majiya karfi aka yi ba, sai dai a nuna mana na’urorin zamani. To da wani dalili za a ce ba za mu iya noma abin da za mu ci ba, har sai an kawo mana daga wata kasar dabam? Wannan ya dogara ne bisa rashin kan-gadon shugabanninmu, wdanda Turawan Yammacin duniya ke daurewa gindi ana zaben su ko ta halin kaka, don su ci gaba da tsiyata kasarsu na haihuwa, kasashen Turawa kuma na ta bunkasa. Wai shin yaushe ne kan mage zai waye?

Saturday, 8 September 2012

A Bari Ya Huce Shi Ke Kawo Rabon Wani


 Wahalar neman albarkatun man fetur a arewacin Najeriya ya fi hakilon bidar allura a cikin rauga. Amma burin ganin an kai ga biyan bukata ba zai zama a banza ba, domin an samu burbushin man a wurare da yawa. An kuma fahimci cewa, haka za ta cimma ruwa, idan aka dukufa sosai wajen tonowa.

Dangane da haka, an ce an samu albarkatu masu tarin yawa a gabar tafkin Chadi, da ke iyaka da kasashen Kamaru da Chadi. An kuma tabbatar da cewa akwai irin wadannan albarkatun malale a gabar kogin Komadugu cikin Jihar Yobe.

To ba wadancan wurare ne kadai Allah ya tarfa wa garinsu nono ba, don a nan Jiharmu ta Bauchi ma, da makwabciyarmu Gombe, an gano cewa akwai dimbin albarkatun man-fetur a karkashin kasa, haka ma an hakikance kan cewa, akwai shi makil, a gabar kogin Binuwai.

To amma, a duk lokacin da aka ce an gano albarkatun mai a wani yanki na Arewa, sai kaga lamarin ya zame tamkar labarin kanzon kurege, musamman ma ga hukumomin gwamnatin tarayya wadanda hakkin tono man da sarrafa shi ya rataya a wuyansu.

Wani babban abin da zai kara ba ka haushi kuma, shine ganin yadda su ma a nasu bangaren, shugabannin mu na nan Arewa, babu wani hobbasa da suke yi game da haka. Hasali ma sun gwammaci su yi ta kasancewa suna dogaro da man kudun da a kullum sai an yi musu gori akai, ana musu kallon cima- zaune, wadanda sai dai su wanke goma su tsoma biyar cikin akushin arzikin kasar da ba sa tsinana komai don karuwarta.

Ko a ranar larabar da ta gabata, sai da muka ji mai girma Gwamnan Jihar Bauchi, Malam Isa Yuguda, ya fito fili yana ta babatu da kame-kame kamar yadda ya saba, a wata tattaunawa da BBC Hausa ta yi da shi. Yana fadin cewa wai kada mutanen Arewa su rika kai kwadayinsu wajen maganar hako man Arewa. Yuguda ya ce, mutanen Arewa mu mai da hankali kan harkar noma kawai, itace kadai hanyar karuwar arziki. Domin a cewar Yuguda, wai burin Gwamnatin tarayya shine sai ta gama kwasan man da ke kudancin Najeriya, sannan za ta karaso, ta ci gaba da wawuson na Arewa. Idan ma abin da Yuguda  ya fada gaskiya ne, to ai an ce teku bata ki Karin ruwa ba. Kuma  guntun gatarin ka ya fi sari ka bani.  Dangane da wannan batu, sai a tambayi Yuguda, shin mara kishin inane shi?

Duk da cewa Gwamnatin tarayya ba ta cewa uffan game da irin dimbin arzikin man-fetur da ake samu a daya daga cikin jihohin Arewa goma sha tara, sai ga Shugaba Jonathan ya kai ziyara Jihar Anambara, inda ya tsoma ta cikin jerin Jihohin da suke da arzikin man-fetur, a matsayi ta goma. A cewar Jonathan, an gano mai a Aguleri Otu, dake yankin karamar hukumar Anambara ta gabas, har ma an kafa wata matatar mai ta musamman don sarrafa danyen man da za a rika hakowa.

To idan haka ne, me yasa bayan sanarwar da tsohon Gwamnan Jihar Kogi Ibrahim Idris ya bayar na cewa an gano man-fetur a jiharsa, Gwamnatin tarayya bata sanar ba, domin a san ainahin wurin da aka gano man, da adadin yawansa, da ingancinsa?

An dai dade da fahimtar cewa akwai albarkatun man-fetur masu tarin yawa a arewacin kasarnan, amma gwamnati bata ko nuna cewa ta san da hakan. Tunda yake dai shiyyoyin Arewaci ne aka gano albarkatun mai, ai ba za a fada ba, kuma babu wani dalilin da zai sanya a tashi haikan don tonowa, tunda dai ba kaunar mu ake da arzikin ba. Amma da yake ana son yi wa Arewa rinton albarkatun man da Allah ya huwace mana, sai gashi ana cewa man da aka gano a Jihar Kogi ma wai na Jihar Anambara ne.

Wannan al’amari ne mai rikitarwa, kuma gwamnatin tarayya ta ja bakinta ta yi gum game da da’awar da Jihar Kogi ke yi, na cewa arzikin man da Jihar Anambara ke tinkaho da shi a Jihar ta Kogin aka samu. Kuma rashin daukar matakan gaggawa don bin bahasin takaddamar da za ta biyo baya game da wannan cece-kuce na iya haddasa rigima tsakanin al’ummomin jihohin biyu, masu makwabtaka da juna.

Idan kuma muka dawo kan batun rashin mayar da hankalin gwamnatin tarayya, game da kin fara hakowa da sarrafa dimbin albarkatun mai da aka gano a wurare da yawa a nan Arewa, za mu fahimci cewa, mu dinne dai al’ummar Arewa baki dayanmu ba a bukatar mu da karuwar arziki.

Suma manya-manyan kasashen yammaci da gabashin duniya, sun kwallafa ransu bisa wannan arziki da Allah ya hore mana. A sabili da haka ne ma, ake ta haddasa yamutsi da rashin kwanciyar hankali a dukkan wuraren da aka tabbatar cewa an samu man-fetur a yankin arewa. Rige-rigen da Kasashen Turai da Amurka ke ta yi don yin kaka-gida su ji dadin tatsa mana arziki, shine ya jawo fitintinun da yanzu haka suka yi kamari a jihohin Borno da Yobe. Da gangan kuma ake jingina su da addini.

To gashi nan al’amarin ya jawo mana bala’i tun kafin ma mu fara cin moriyarsa.

Idan kuma har da gaske Gwamnatin Jonathan ke yi na kara kokartawa don binciken gabar kogunan kasarnan dake kan iyakokin kasashe makwabta, musamman ma a nan arewa maso gabas, to sai ta yi himmar farawa  tun yanzu, domin ance a bari ya huce shi ke kawo rabon wani.

SAKIYAR DA BA RUWA

“Najeriya ce Ƙasar da muke da ita, ba mu kuma da wacce ta fi ta. Wajibi ne mu kasance a cikin ta, mu kuma haɗa kai wajen kyautata makomar...