Wahalar neman albarkatun man
fetur a arewacin Najeriya ya fi hakilon bidar allura a cikin rauga. Amma burin
ganin an kai ga biyan bukata ba zai zama a banza ba, domin an samu burbushin man
a wurare da yawa. An kuma fahimci cewa, haka za ta cimma ruwa, idan aka dukufa
sosai wajen tonowa.
Dangane da
haka, an ce an samu albarkatu masu tarin yawa a gabar tafkin Chadi, da ke iyaka
da kasashen Kamaru da Chadi. An kuma tabbatar da cewa akwai irin wadannan
albarkatun malale a gabar kogin Komadugu cikin Jihar Yobe.
To ba
wadancan wurare ne kadai Allah ya tarfa wa garinsu nono ba, don a nan Jiharmu
ta Bauchi ma, da makwabciyarmu Gombe, an gano cewa akwai dimbin albarkatun
man-fetur a karkashin kasa, haka ma an hakikance kan cewa, akwai shi makil, a
gabar kogin Binuwai.
To amma, a
duk lokacin da aka ce an gano albarkatun mai a wani yanki na Arewa, sai kaga lamarin
ya zame tamkar labarin kanzon kurege, musamman ma ga hukumomin gwamnatin
tarayya wadanda hakkin tono man da sarrafa shi ya rataya a wuyansu.
Wani babban
abin da zai kara ba ka haushi kuma, shine ganin yadda su ma a nasu bangaren,
shugabannin mu na nan Arewa, babu wani hobbasa da suke yi game da haka. Hasali
ma sun gwammaci su yi ta kasancewa suna dogaro da man kudun da a kullum sai an
yi musu gori akai, ana musu kallon cima- zaune, wadanda sai dai su wanke goma
su tsoma biyar cikin akushin arzikin kasar da ba sa tsinana komai don
karuwarta.
Ko a ranar
larabar da ta gabata, sai da muka ji mai girma Gwamnan Jihar Bauchi, Malam Isa
Yuguda, ya fito fili yana ta babatu da kame-kame kamar yadda ya saba, a wata
tattaunawa da BBC Hausa ta yi da shi. Yana fadin cewa wai kada mutanen Arewa
su rika kai kwadayinsu wajen maganar hako man Arewa. Yuguda ya ce, mutanen
Arewa mu mai da hankali kan harkar noma kawai, itace kadai hanyar karuwar
arziki. Domin a cewar Yuguda, wai burin Gwamnatin tarayya shine sai ta gama
kwasan man da ke kudancin Najeriya, sannan za ta karaso, ta ci gaba da wawuson na
Arewa. Idan ma abin da Yuguda ya fada
gaskiya ne, to ai an ce teku bata ki Karin ruwa ba. Kuma guntun gatarin ka ya fi sari ka bani. Dangane da wannan batu, sai a tambayi Yuguda,
shin mara kishin inane shi?
Duk da cewa
Gwamnatin tarayya ba ta cewa uffan game da irin dimbin arzikin man-fetur da ake
samu a daya daga cikin jihohin Arewa goma sha tara, sai ga Shugaba Jonathan ya
kai ziyara Jihar Anambara, inda ya tsoma ta cikin jerin Jihohin da suke da
arzikin man-fetur, a matsayi ta goma. A cewar Jonathan, an gano mai a Aguleri
Otu, dake yankin karamar hukumar Anambara ta gabas, har ma an kafa wata matatar
mai ta musamman don sarrafa danyen man da za a rika hakowa.
To idan
haka ne, me yasa bayan sanarwar da tsohon Gwamnan Jihar Kogi Ibrahim Idris ya
bayar na cewa an gano man-fetur a jiharsa, Gwamnatin tarayya bata sanar ba,
domin a san ainahin wurin da aka gano man, da adadin yawansa, da ingancinsa?
An dai dade
da fahimtar cewa akwai albarkatun man-fetur masu tarin yawa a arewacin
kasarnan, amma gwamnati bata ko nuna cewa ta san da hakan. Tunda yake dai
shiyyoyin Arewaci ne aka gano albarkatun mai, ai ba za a fada ba, kuma babu
wani dalilin da zai sanya a tashi haikan don tonowa, tunda dai ba kaunar mu ake
da arzikin ba. Amma da yake ana son yi wa Arewa rinton albarkatun man da Allah
ya huwace mana, sai gashi ana cewa man da aka gano a Jihar Kogi ma wai na Jihar
Anambara ne.
Wannan
al’amari ne mai rikitarwa, kuma gwamnatin tarayya ta ja bakinta ta yi gum game
da da’awar da Jihar Kogi ke yi, na cewa arzikin man da Jihar Anambara ke
tinkaho da shi a Jihar ta Kogin aka samu. Kuma rashin daukar matakan gaggawa
don bin bahasin takaddamar da za ta biyo baya game da wannan cece-kuce na iya
haddasa rigima tsakanin al’ummomin jihohin biyu, masu makwabtaka da juna.
Idan kuma
muka dawo kan batun rashin mayar da hankalin gwamnatin tarayya, game da kin
fara hakowa da sarrafa dimbin albarkatun mai da aka gano a wurare da yawa a nan
Arewa, za mu fahimci cewa, mu dinne dai al’ummar Arewa baki dayanmu ba a
bukatar mu da karuwar arziki.
Suma
manya-manyan kasashen yammaci da gabashin duniya, sun kwallafa ransu bisa
wannan arziki da Allah ya hore mana. A sabili da haka ne ma, ake ta haddasa
yamutsi da rashin kwanciyar hankali a dukkan wuraren da aka tabbatar cewa an
samu man-fetur a yankin arewa. Rige-rigen da Kasashen Turai da Amurka ke ta yi
don yin kaka-gida su ji dadin tatsa mana arziki, shine ya jawo fitintinun da
yanzu haka suka yi kamari a jihohin Borno da Yobe. Da gangan kuma ake jingina
su da addini.
To gashi
nan al’amarin ya jawo mana bala’i tun kafin ma mu fara cin moriyarsa.
Idan kuma
har da gaske Gwamnatin Jonathan ke yi na kara kokartawa don binciken gabar kogunan
kasarnan dake kan iyakokin kasashe makwabta, musamman ma a nan arewa maso
gabas, to sai ta yi himmar farawa tun yanzu,
domin ance a bari ya huce shi ke kawo rabon wani.
No comments:
Post a Comment