Tuesday, 14 August 2012

Komi Aka Yi Da Jaki Sai Ya Ci Kara


Cif Edwin Kiagbodo Clark dan siyasa ne mai fada aji a yankin Neja-Delta. Inda duk dattijo ya kai, ana iya cewa ya kai, amma sai dai bai iya bakinsa ba. Ga shi ya manyanta matuka, ‘yan shekaru kadan suka rage ya cika casa’in, amma dabi’u da take-takensa irin na tsohon Najadu ne. Hasali ma a duk lokacin da Cif Edwin Clark ya buda baki, ya yi furuci, za ka ji kamar kasa za ta tsage, za ka ji kowa na Allah-wadai da shi, don kuwa kalamansa ko kare ma ba zai ci ba. Alheri ba ya taba  fitowa daga bakinsa, sannan maganganunsa ba yawa ba dadi.
Siyasar kabilanci ce babbar dabi’arsa, da ita yake ci, yake sha, yake kuma takama. Wannan ne ya sa Edwin Clark ya yi fice a karkararsu, ya kuma yi kaurin suna a kwaryar tarayyar Najeriya. Shine ya nada kansa da kansa mukamin Jagorar kungiyar Dattijan Neja-Delta. Kabilarsu daya da ta shugaba Jonathan, amma baya kaunarsa, domin ba irin kutun-kutun din da bai yi wa Jonathan ba don kar ya zamo shugaban kasa. Bayan abin ya sha karfinsa sai kuma ya komo ba shi da wani gwani kamar Jonathan.
Ba abin da Edwin Clark ya sanya gaba, sai sake-kake, da kulle-kullen yadda Kabilar Ijaw za ta tsere, ta yi fin-tin-kau wa sauran kabilun yankin Neja-Delta. Ya tsani ‘yan kabilar Itsekiri. Shi yasa ma a 2007 ya fito karara ya nuna kin amincewarsa da tsayawa takarar Emmanuel Eduaghan a matsayin gwamnan Jihar Delta, don kabilarsu daban-daban ne. Inda ma Cif Edwin Clark ya fi kaurin suna a ‘yan kwanakin nan, shi ne wajen kokarin rushe tubalin ginin da ta hade kan ‘yan Najeriya, don Kasar ta ci gaba da rushewa.
Dangane da haka, yanzu Cif Edwin Clark shine kan gaba wajen nuna kyama da kiyayya ga yankin Arewa da shugabanninta da kuma ‘ya’yanta. A kullum jikinsa kaikayi yake masa har idan bai kalkalo wata jafa’in da zai malkaya wa ‘yan Arewa ba. Burinsa a ko da yaushe shine, ya kalato kashin-kajin da zai shafa wa ‘yan Arewa don ya bakantamu a idanun iyayen gidansa na kasashen ketare, masu kyamar jama’ar arewa da abin da muka yi imani da shi.
A halin da ake ciki yanzu lamarin Cif Edwin Clark ya faskara, ya fara wuce gona da iri, shi yasa ma a ‘yan kwanakin nan ya dauki karan-tsana ya dora wa gwamnonin jihohin Arewa da tsofaffin shugabannin kasar ‘yan asalin Arewa, ba domin komai ba, sai don ya tayar da zaune tsaye, ya ruruta wata wutar fitinar da za ta karasa daidaita kasar.
Akan haka ne, a wajen wani taron kungiyar lauyoyi a Abuja, ranar larabar makon jiya, Edwin Clark ya hakikance cewa wai gwamnonin Arewa ne suka kafa kungiyar Boko-Haram domin kawai su dagula lissafin gwamnatin Jonathan. Clark yayi amannar cewa wasu ‘yan Arewa ne da Jonathan ya kayar a zaben 2011, masu alaka da kungiyar Boko-Haram su ke hure kurwar gwamnatin Jonathan suke haddasa fitintinu iri-iri. Ya kuma kara da zargin wasu da ya kira ‘yan koren da kungiyar gwamnonin Najeriya ta kafa cikin manyan kwamitocin jam’iyyar PDP na kasa, wai su ke dafa wa gwamnonin Arewar don kai Jonathan kasa. A cewarsa gwamnonin Arewa sun karkata akalar jam’iyyar PDP zuwa inda suke so, sun kuma turketa a can, sai yadda suka ga dama suke yi da ita.
To tun da yake abin na Edwin Clark rainin wayo ne da rashin ta ido, sai gashi ya fito balo-balo yana kalubalantar Janar Buhari, da Janar Babangida da su fito fili su wanke kawunansu daga zargin da yake musu, na cewa suna da ruwa da tsaki game da tashe-tashen bama-bamai da suka ki ci suka ki cinyewa a arewacin Najeriya. Ya ce wai su fito kiri-kiri su nuna wa al’ummar kasar cewa ba su da wata alaka ko dangantaka da kungiyar Boko-Haram. Ba irin kalaman tozartawa da Edwin Clark bai furta ba. Ya ce wai shugabannin arewa ba wanda ya taba kai ziyara jihar Borno, don tausayawa jama’ar da ‘yan Boko-Haram suka addaba, sai Janar Olusegun Obasanjo ne kadai ya kai ziyara garesu don jajanta musu.
‘Yan magana suka ce gajerar kuka dadin hawa gareta. Shin Edwin Clark ya manta cewa Shugaba Jonathan ma bai taba zuwa ko’ina ba a Arewa don jajantawa ga jama’ar da bala’in jefe-jefen bama-bamai suka tagayyara ba? Tsakanin shi da su Buhari wanene ya wajaba a kansa yayi tattaki zuwa Jihar Borno don jajantawa da ba da tallafi wa wadanda rigimar ta shafa?
 Sanin kowa ne, inda Jonathan ke son kai ziyara bayan an shirya harin ta’addanci ya kai, an kuma san wadanda ya je domin su, da kuma dalilan da suka sa yaje din, sune kuma kadai wadanda aka taba biyan diyya bayan an kaddamar da ta’ddancin harin bam. A game da batun manyan arewar da yake zargin sun ki cewa uffan game da bala’o’in Boko Haram, sai a tambayi Cif Edwin Clark, shin yana so ne su yi ikirarin su ne iyayen gidan ‘yan Boko-Haram din? Ko so yake yi su ce da sanin su ake  tafka ta’asar da yake zargin suna haddasawa don su faranta masa rai?
To har dai idan Cif Edwin Clark ba so yake ya bata arewa da shugabanninta ba ne, ai ya sani sarai cewa sun sha fitowa suna kalubalantar ‘yan kungiyar Boko-Haram, da nuna musu cewa abin da suke yi baya da nasaba da addinin musulunci. Ai ko ba komai ba za su daura yaki su ci kasarsu ba. Yanzu wani bangaren kasar nan ne gari ya waya game da masifun da tashin hankalin Boko-Haram ke haddasawa? Arewa da jama’ar cikinta mune kawai muke kwaruwa musamman ma mu ‘yan arewa maso gabas (North East), sauran ‘yan Najeriya kuwa ko a jikinsu, ba su damu da haka ba. A ganinsu tun da dai jifa ta wuce kansu, to ta ma fada kan uban kowa mana.
 Zarge-zargen da Edwin clark yake wa su Janar Buhari ko kadan basu da makama ballantana tushe. A,a, to idan kura na da maganin zawo me zai hana ba za tayi wa kanta ba? ‘yan arewa da wasu daga cikin shugabanninmu mun fi kowa damuwa game da haka, sai dai babu abin da muka iya. Wadanda daga cikinmu za su iya tabukawa don hanawa da magancewa, su kuma ba ruwansu, matukar ba cikin gidajensu ake jefa bama-bamai ba, sun ma fi gwammacewa al’amuran su ci gaba da tabarbarewa.
A game da gwamnonin Arewa da Edwin Clark ya shafa wa kashin-kaji kuwa, sai ace da su Allah ya kara, ga irinta nan ai. Ba su ne suka saki na hannu suka bi na dawa ba? Suka saki reshe suka kama ganye? Yanzu sun gane cewa da ruwa ake shayi, domin irin sakamakon da aka yi musu kenan, bayan da suka tayar da kura a zaben watan afrilun bara, suka yi amfani da addini  da kabilanci, suka tayar da husumar da ta yi sanadiyyar asarar rayuka da dimbin dukiyar al’umma, suka kuma jingina laifin tayar da tarzomar wa wasu manyan arewa.
Daga karshe kuma ga shi nan ‘yan kudun da suka yi wa gata, sun ci, sun goge bakunansu. Tunda yake sun ci moriyar ganga, to yanzu sakayyarsu ga ‘yan arewa ita ce ta rainin wayo da neman ganin bayansu. A game da halin Edwin Clark kuwa, da halayen irin su Alhaji Mujahid Asari Dokubo, da ma sauran ‘yan kudancin Najeriya, mu ‘yan arewa ba mu da ta cewa, domin ance komai aka yi da jaki sai ya ci kara.

No comments:

Post a Comment

SAKIYAR DA BA RUWA

“Najeriya ce Ƙasar da muke da ita, ba mu kuma da wacce ta fi ta. Wajibi ne mu kasance a cikin ta, mu kuma haɗa kai wajen kyautata makomar...